A tuntube mu a 08061654483

Name

Email *

Message *

Friday, 27 April 2018

Falalar watan Azumi

FALALAR WATAN AZUMIN RAMADAN DA IRIN
ROMON DA YAKE CIKINSA.
TAMBAYA ???
MENENE FALALAR WATAN AZUMIN
RAMADAN ???
AMSA
-----
Azumin Ramadan yanada falaloli da yawa.
Daga cikin falalar azumin sun hada da:-
1. Yana kankare zunubin mutum kamar yadda
yazo a hadisin Khuzaifah (R.A.) Yace:
Manzon Allah {S.A.W} yace:
"Fitinar mutum acikin iyalansa, da dukiyarsa ko
makwabcinsa sallah da azumi da sadaka suna
kankaresu (Bukhari).
2. Yazo a hadisai da dama cewa:
Dukkan aikin Dan Adam nasane Malaikune suke
rubuta shi, amma azumi wannan na Allah ne Shi
Yake sakawa wanda yayi shi (hadisin ya tabbata
acikin targhib wattarhib, juz'I na farko shafi na
75).
3. Hadisi kuma ya tabbata daga Jabir dan
Abdullahi (R.A.) daga Manzon Allah {S.A.W.}
cewar:
Azumi garkuwane da dan Adam zaiyi garkuwa
dashi daga wuta.
3. Sannan hadisi ya tabbata daga Mu'azu dan
Jabal (R.A.) cewa:
Hakika Manzon Allah {S.A.W.} yace dashi shin
bazan nuna maka kofofin alheriba ?
Sai yace na'am ya Rasulullah.
Sai yace azumi garkuwane.
4. Sannan akwai hadisin Abi Umamata (R.A.)
yace:
"Nacewa Manzon Allah (s.a.w) ka umarceni da
wani aiki da Allah Zai amfanar dani dashi sai
yace ka lizimci azumi, domin babu kamarsa"
(dukkan wadanna hadisai sun tabbata a targhib,
tahakikin Sheikh Albani juzu'I na farko shafi na
578).
6. Azumi kuma shine sababin tsoron Allah.
7. A lokacin azumin Ramadan ana bude kofofin
Aljanna, kuma ana kulle kofofin Jahannama
sannan a daure shaidanu kamar yadda ya
tabbata a hadisin Abi Huraira.
(Kuduba Sahihul Bukhari 1899).
8. Hadisi ya tabbata wanda Imam Tirmizi ya
ruwaito cewar Manzon Allah {S.A.W.} yace:
"Warin bakin mai azumi yafi kamshi fiye da
turaren Al-miski a wurin Allah.
Hadisine sahihi.
9. Sannan wani hadisin ya tabbata daga Sahl bin
Sa'ad (R.A) daga Manzon Allah {S.A.W.) yace:
Acikin Aljanna akwai wata kofa ana kiranta
Rayyanu, masu azumi zasu shigeta ranar tashin
kiyama, babu wanda zai shigeta sai su.
Idan sun shiga sai a kulleta babu wanda zai sake
shiga
(Kuduba Sahihul Bukhari 1896).
Tirmizi yakara bayani a cikin riwayarsa cewar
wanda ya shigeta bazaiji kishin ruwaba (Qishirwa
ba) har abada. Allah ya Albarka ci rayuwar mu ya
mana jagoranci yasa albarka a cikin karatun mu yasa
sauki a ciki yasa muna daga cikin bayin da zaa yanta a
wannan wata mai Albarka

An kashe musulmai 27 a jihar Benuwai

Matasan Kiristoci Sun Kashe Musulmai 27 Tare Da Kona Masallatai Biyu A Jihar Binuwai
Rahotanni sun nuna cewa akalla mutum 27 ne aka kashe, yayin da wasu da dama suka jikkata a rikici na baya-bayan nan a Makurdi, babban birnin jihar Benue.
An kuma kona masallatai da kuma hasarar dukiya a harin wanda ake zargin na ramuwar gayya ne da ake zargin 'yan kabilar Tivi da kai wa Hausa/Fulani.
Wadansu da suka ga lamarin sun shaida wa BBC cewa wadansu gungun mutane ne suka "tare hanyoyin cikin gari tare da tsare mutane, inda suka rinka kashe su."
Rundunar 'yan sandan jihar ta ki cewa uffan kan bukatar da BBC ta mata na yin magana kan lamarin. Shi ma sakataren yada labaran gwamantin jihar, Terve Akase, ya ce ba shi da labarin harin.
Sai dai wani Basarake na kabilar Tivi, wadanda aka zarga da kai harin, ya ce suna iya kokarinsu domin ganin ba a kai hare-haren ramuwar gayya ba.
Wani dalibi da ya shida lamarin wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce da idanunsa ya ga yadda gungun mutane suka "tare hanyar zuwa jami'ar garin kusa da wani asibiti suna tare mutane su doke su, kana kuma kuma su yi musu kwace sannan su kashe su."
Dalibin ya kara da cewa "Hausawa ne ko Musulmi ake yi wa hakan."
Shi ma babba limamin masallacin Izala na birnin, Sheikh Shu'aibu, ya shaida wa BBC cewa, da idanunsa ya ga "gawawwakin Musulmi da aka kashe 27" a asibitin koyarwa da ke birnin.
Limamin ya ce an ji wa wadansu "Musulmin rauni da dama," ba ya ga wadanda ba a gansu ba kuma.
Sheikh Shu'aibu, ya ci gaba da cewa, an "kona wadansu masallatai guda biyu" wadanda aka gyara su bayan an kona su a rikicin baya.
Sheikh Sha'aibu ya ce yanzu dai abin ya dan lafa, kuma dama lamarin dai yafi kamari ne a wajen birnin.
To sai kuma shugaban kabilar Tivi, Tar Makurdi Chief Sule Abenga, ya shaida wa BBC cewa:
"Na san cewa akwai zaman dar-dar a Makurdi, tun bayan da aka kashe wadansu limaman coci da wadansu Kiristoci, alamu suka nuna cewa za a iya daukar fansa,"
Ya ci gaba da cewa: "amma mun yi bakin kokarinsu don tabbatar da ganin hakan bai faru ba. Kuma shi bai san cewa mutanensu na aikata irin wannan ta'asa ba."
Matashiya.
Wannan zaman dar-dar din ya samo asali ne tun a ranar Talatar da ta gabata lokacin da ta bayyana cewa wadansu 'yan bindiga da ake zargin makiyaya ne sun shiga wata majami'a a wani kauye karkashin karamar hukumar Gwer.
Maharan sun kuma bude wuta irin ta kan mai uwa da wabi, al'amarin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum 17 ciki har da limaman coci biyu.
Rikicin manoma da makiyaya dai a Najeriya ya yi sanadin asarar rayuka daga dukkan bangarorin biyu.
Rikicin ya fi kamari ne a jihohin Filato da Benue da Taraba da Nassarawa da Kaduna.
A baya gwamnatin tarayya ta yi kira ga gwamnonin jihohin da lamarin ya shafa su samar da wuraren kiwo.
Sai dai gwamnonin sun yi fatali da wannan bukata, suna masu cewa ba su da isassun filayen da za su bayar.

Za,a Kafa dokar tabaci a benuwai

Majalisa Ta Nemi A Kafa Dokar Ta- Baci A Binuwai
▪ Ana Ingiza Rikicin Binuwai Ne Don A Raba Nijeriya — Buhari
_____¥____
*
Majalisar Dattawa ta kalubalanci Shugaba Muhammad Buhari kan ya kakaba dokar ta-baci a jihar Binuwai don ganin an kawo karshen zubar da jini da ake yi sakamakon rikicin makiyaya da manoma.

A nasa bangaren, Shugaba Buhari ya jaddada cewa masu Ingiza rikicin jihar Binuwai na neman wargaza Nijeriya inda ya gargadi al'ummar jihar kan su yi takatsantsa da makiyan kasar nan wadanda ke ingiza su kan kashe junansu.

Saturday, 21 April 2018

Ya Kamata Buhari Ya Bar Wani Mai Kwazo Ya Karbi Mulki — Sheik Gumi ___¥___

Fitaccen malamin addinin Musuluncin nan, Shekh Ahmad Gumi ya bayyana cewa kokarin da Shugaba Buhari ke yi bai Wadaci al'ummar Nijeriya ba don haka ya kamata ya bari wani sabon jini mai kwazo ya ci gaba da jan ragamar mulkin kasar nan.

Malamin ya kwatanta mulkin Buhari da wani dalibinsa wanda ke da kokari jajircewa wajen nazari amma kuma ba ya cin jarrabawa inda malamin ya yi bayanin cewa iyakacin hazakar dalibin kenan ba wai rashin kokari ba ne. Sheik Gumi ya tabbatar da cewa Buhari yana kokari amma kuma kokarin nasa bai iya biyan bukatun 'yan Nijeriya ba.

Mun gama da Boko Haram: Janar Buratai ya sake nanatawa ga duniya

- Buratai ya tabbatar da cewa an fi karfin Boko Haram, an shirya hada kan 'yan gudun hijira

- Duk da' yan kunar bakin wake a Arewa maso gabas, sojojin Najeriya a ranar Alhamis sun ce a fatattaki kungiyar Boko Haram

- "Daukacin rundunar sojojin zasu koma Borno don dawo da wadanda suka bar ta sannan zamu zauna dasu na wata hudu ko biyar"


Mun gama da Boko Haram: Janar Buratai ya sake nanatawa ga duniya
Shugaban sojojin Lieutenant General Tukur Buratai, ya fadi haka a tataunawar waya da yayi da manema labarai. Wanda, taron United States Mission, Nigeria to wrap up the African Land Forces, 2018 ta shirya da hadin guiwar kwamandan US Army Africa, Gen. Eugene LeBoeuf.

Yace ana shirye shiryen maida 'yan gudun hijirar zuwa garuruwansu a Borno. 'Yan gudun hijirar da suka tsere suka bar guraren zaman su sakamakon hare haren 'yan Boko Haram, za a maida su gidajen su tare da tsaron sojoji na wata hudu ko biyar "

A lokacin da wani manemin labarai ya tambayeshi cewa duk da sojojin suna kara tabbatar da cewa an fatattaki 'yan ta'addan amma bashi yasa aka daina Jin tashin hankalin da suke haddasawa ba.

Yace "Da farko dai ka duba daga inda muke, ina muke da kuma ina zamu je. A da Boko Haram suna walwalar su a duk inda suke so a fadin kasar nan. Kafin 2015, sun kai Abuja, Lokoja, Sokoto, Kano, Kaduna, Jos, Bauchi".

Kai a takaice ma duk sassan kasar nan ballantana arewa da wasu sassan tsakiyar kasar. Amma tun 2016 babu harin da aka kaiwa wajen arewa maso gabas. A 2017, babu wani babban hari da aka kai Arewa maso gabas. A wannan lokacin kuwa nasan zaku yarda cewa mun fi karfin Boko.

"In dai a Maiduguri kake ko wani sassan na arewa maso gabas, zaka yarda cewa Boko Haram ta mutu. A shekaru biyu da suka wuce bama dajin sambisa amma yanzu muna cikin shi"

"A iya sanina, nasan mun fatattaki Boko Haram, mun wuce nan. Wasu ma daga cikin 'yan gudun hijira sun fara komawa garuruwansu."

Yadda ake bude gmail Account

Sau da yawa mutane kan so su yi wani abu a saman internet, kamar buder account na website, da dai sauransu, amma rashin e-mail sai ka ga yana hana su yin wannan abu. Akwai da dama daga cikin mutance da ke turo mana da koken cewa su sun kasa bude e-mail account duk da kuma cewa sun yi iya bakin kokarinsu.

A cikin wannan kasida tamu ta yau, zama nuna muku hanyar da zaku bi a saukake domin bude e-mail (gmail). Amma ya kamata ka sani cewa, yafi matukar sauki sosai ka bude gmail da computer a maimakon yin amfani da waya. Zaka iya zuwa a kowace Café, minti goma ya ishe ka. Amma idan har baka iya samun damar yin amfani da computer, zaka iya amfani da waya (musamman ma android).

Ga wadannan matakai kamar haka:

Ka shiga website din gmail.com
Sai ka shiga wajen create new account
Wannan zaya kai ka zuwa inda zaka shigar da bayananka. Sai ka shigar da su kamar haka:

Bayan ka gama sai ka danna “Next Step”. Daga nan wani shafi zaya fito wanda zaya bukaci ka amince da sharudan google:

Daga nan zaka wuce  zuwa inda za’a bukaci kayi verifying din lambar wayarka. Sai ka zabi hanyar da kafi bukata, ko ta kira ko kuma ta message.

Idan ka sun baka code din (ta hanyar kira ko kuma ta hanyar message) Sai ka sanya a cikin wajen da zasu samar maka da shi (Kamar yadda zaka iya gani a cikin foton):
Da zaran kayi verirying ko kuma tabbatar da lambar wayarka zasu nuna wannan page da ke nuna cewa ka kammala komai.


Amma idan da waya zaka yi amfani, to tun a farko zaka fara sanya lambarka  ne sai su turo maka da wani link ta message. Wannan link din shine matayin verification code da zasu turo maka(idan kayi amfani da computer). Wannan link shi zaka bi domin ci gaba da rajistar.

Wadanan sune matakan da kake bukatar domin bude gmail accoount da kanka ba tare da ka baiwa wani kudi ba domin ya yi maka.

Comedy

Conversation Between NEPA & Fire Service:

*NEPA*:  Hello, fire service, please we need help. Our office is on fire.

*Fire Service*: sorry, We don't have light to pump water
😂😂😂😂

Tuesday, 17 April 2018

Comedy

Teacher: who is the president of Nigeria?
Children: Nnamdi Azikiwe
Teacher: good!!
Who is the minister of defence?
Children: Bukola Saraki
Teacher: correct!!
What is the capital city of Nigeria?
Children: Benin City
Teacher: very good!!
Who composed the national anthem?
Children: Timaya
Teacher: Excellent!!
If the people from Nigeria are called Nigerians,
How will you call the people from Moscow?
Children: Mosquitoes
Teacher:wow!!
Then, 2+5 will give you wat?
Children: 25
Teacher: perfect!!
You will remain stupid like
this until Your Governor pays my salary.

Don't spoil the fun, send it to ur friends.😂😂😂